+22780416252
*Page 03*
Da ido na kafe Sumayya ina sakin murmushi a ƙasan zuciyata wanda a zahiri kuwa duk na yi kicin-kicin da fuskata alamar ban ji daɗin abin da yake faruwa ba. Miƙo min jakar Rumana ta yi ta ce"Mama ga jakar ki duba" wani shu'umin murmushi na yi na ce"Ba Abdallah, shi ne mijinta shi ya fi dace wa da ya buɗe don gani da idonshi" karbar handbag ɗin Abdallah ya yi ya shiga buɗe ta ya fara fito da kayan ciki. Sumayya kuwa ta yi tsaye tana kallon shi har yanzu abin da nake burin gani bai faru ba don na matsu na ga hawaye suna zuba daga wannan kyakkyawar fuskar ta Sumayya. Kuɗin ya ciro ya shiga juya su a hannunsa fuskarsa ɗauke da damuwa ya ce"Mama mutumin da ya kawo kuɗin nan bai faɗa miki sunansa ba?" Girgiza kai na yi na ce"A a kawai dai ya bani sakon da zan faɗa mata ne kuma na faɗa mata" sai yanzu Malam ya yi magana ya ce"Sumayya ƴata me ya faru? Kin san mutumin da ya kawo kuɗin nan?" Saurin amshe zancen na yi ta hanyar cewa "Ku ji malam da wata magana, kenan ni ba ku yarda da abin da na faɗa ba shi ne sai ka ji ta bakinta" "To Sa'a ai ba haka ake shari'a ba, ko ba komai kin tsaya mu ji abin da yarinya za ta faɗa don sanin gaskiyar magana kila rashin fahimtar zancen mutumin ne kika yi" har na buɗe bakina don yin magana sai na ji Abdallah na faɗi "Babe, ke muke jira mu ji wane ne ya kawo miki kuɗi har gida?" A ɓoye na sauke wata ajiyar zuciya don ganin yadda ran Abdallah ya ɓaci yau kam babu shaka sai Sumayya ta tafi gidansu.
★Sumayya★
Da mamaki nake bin su da kallo, raina ya kai kololuwa wajen ɓaci, wani irin ɗaci nake ji a cikin raina wanda na rasa ta ina zan fara kwatanta shi. Da ido nake bin hannun Abdallah da kallo yadda har yanzu yake juya kuɗin yana wani zare ido tamkar bai san daga ina kuɗin suka fito ba. Daƙyar na iya daukar dutsen jarumta na ɗaura akan bangon zuciyata wajen hana hawayen baƙin cikin da ya yi kawanya a cikin zuciyata zubo wa a gaban idonsu. "Ke fa muke jira ko" Muryar mijina ta daki kunnena buɗe bakina na yi daƙyar na ce"Ba abin da kuke tunani ba ne, kuma kuɗin da ake magana akan su tun daga office na zo da su" wani tsalle Mama ta yi tare da fashewa da wani irin kuka wanda za ka iya rantse wa da Allah naman jikinta ake yanka ta ce"Sumayya yanzu ƙarya zan yi miki kenan? Ba laifinki ba ne idan da ni na haife ki ai ba za ki kalli idona ki ce na yi karya ba, amman sanin ba ni da daraja a idanun ki dole ki faɗi haka"
Tuni hankalina ya ƙara tashi don na san a kaf duniyar nan idan akwai abin da yake ɓata ma Abdallah rai ya ga mahaifiyarsa cikin damuwa, musamman da yanzu da ba lafiyar kirki gare ta ba "Mama ki yi hakuri ba abin da nake nufi ba..." Ban ƙarasa maganar da na fara ba Abdallah ya ɗaga min hannu ya ce"Babe je ki ɗaki ina zuwa" ban kuma ƙara faɗar wata magana ba na bar dinning din don zuwa ɗakina.
Isa ta ɓangarena ban yi tsinke ba sai a ɗakina na zube a tsakiyar gadona tare da fashewa da kuka wanda ya riga ya zamar min abin yi. Na dauki lokaci mai tsawo a wajen kafin Abdallah ya turo ƙofar ɗakin ya shigo tare da sallama, ban samu damar amsa wa ba don har yanzu hawaye na zarya daga idanuna ga bangaren kaina na dama da ya ɗauki wani uban ciwo kamar ana buga min guduma a wajen.
Zama ya yi a bakin gadon tare da ajiye handbag ɗin da na baro musu ita a falo, hannu ya saka ya fara share min hawaye ya ce"Ki yi hakuri Babe na yarda da ke ɗari bisa ɗari sai dai kuma kin riga da kin san ba zan iya ƙaryata mahaifiyata ba a gaban idonta kuma a gaban ƴan uwana" rinanun idanuna na watsa mishi na ce"To na ji, amman ko ba komai bai dace ka yi min tsawa akan laifin da ban aikata shi ba" tausasa muryarsa ya yi ya ce"Na sani amman a lokacin na rasa abin yi ne, amman don Allah ki yi hakuri ki min afuwa kin ji matata" gyaɗa kaina na yi na ce"Ya wuce, amman ina son ka fice min daga ɗaki zan yi barci" "yau a nan zan kwana" ban ko kalle shi ba na ce"ga waje nan sai ka kwanta" ina gama maganar na shige toilet a can ɗin ma sabon kukan da babu mai rarrashina na kuma ɗaura shi daga inda na tsaya.
Ganin dai Sumayya ba ta niyyar fitowa daga toilet din sai ya tashi ya tafi ɗakinsa ya canza kaya kafin ya dawo ɗakin sumayya ya bi lafiyar gado.
Washegari ban yi la'akari da abin da ya faru a daren jiya ba, na fito zuwa kitchen don girka abin da za mu ci, yau cike da mamaki nake bin Mama da ƴaƴanta da ke zaune a falo suna ta faman hira da kallo. Gaishe ta na yi kafin na juya na fara kokarin barin falon don yin abin da yake gabana sai Jiddah ta ce" Anty Sumayya a cikin kuɗin da saurayinki ya ba ki jiya ki bani 20k mana", babu kunya babu tsoron Allah ta ƙarasa maganar tana wani juya idanu ko kallo ba ta ishe ni bare kuma ta saka ran zan amsa mata na bar falon ban ce ko uffan ba.
Ko da na gama aikin gabana na haɗa abincin Abdallah don kai shi ɗakinmu har zan wuce Mama ta ce"Idan ba za ki zauna ki ci abinci kamar kowa a dinning ba kar ki kuskura ki ƙara shigar min da abinci zuwa ɓangarenku" ban yi magana ba na koma na ajiye kwanukan akan dinning kafin na haura sama na tarar da shi har ya gama shirinsa da dukan alamu ni ɗaya yake jira. Zama na yi a bakin bed na gaishe shi na ce"Qalbi yau kam ka sauka ƙasa ka yi breakfast" yana gyara zaman rigar suit ɗin da ke jikinsa ya ce"Akan wane dalili bayan kin san sarai na fi son na yi breakfast ɗina a falona" murmushi na yi na ce"Haba Qalbi iya na yau ne fa kaɗai, gobe ma idan Allah ya kai mu a nan za ka ci ka ƙoshi" "to shi kenan na amince amman na yau kaɗai" gyaɗa kaina na yi a cikin raina na ce"yau ɗin idan na guje wa masifar Mama ai na isa barka" da sauri na ɗago kaina don jin Abdallah yana magana sai na ce"Idan ka gama mu je ka karya ko?" Sai da ya bi ni da kallo tun daga ƙasa har sama kafin ya ce"Ban fahimta ba za ki je office ba ne yau ko mene ne?" Girgiza kai na yi na ce"Me ka gani, zan je mana" "don na ga ba ki shirya ba har yanzu" "mu je idan ka gama cin abinci zan dawo sai na shirya"
Ƙasa muka sauko har mun fara taka steps ɗin gidan ya ce"Wai da yaushe kike breakfast Babe? Kullum sai dai ni na ci ke ba za ki ci abin da kika girka da kanki ba" murmushi wanda ya fi kuka ciwo na yi don jin maganar Mama Sa'a ta wancan ranar na yi daram a cikin kwanyata.
"Babu abin da kika iya daga ki ci sai dai ki kai toilet ki zubar, shekara uku da aure amman shiru malam ya ci shirwa ko ɓatan wata ɗaya babu" jin Abdallah ya dafa kafaɗa ta ne ya saka na dawo daga duniyar tunanin da na lula na ce"Ina cin abinci mana kawai dai ba na son yin breakfast ɗin ne tun safe don kar na je office na yi barci" gyaɗa kai ya yi bai ce komai amman alamun shi sun nuna bai yarda da abin da na faɗa ba, ni kuwa han wani damu ba na ja shi muka ƙarasa dinning din na zuba mishi abinci ya shiga ci. Yana gama wa ya shiga ɗakin Mama ya gaishe ta kafin ya fito ya same ni a wajen da ya bar ni, ya ce"Babe kuɗin da na gani jiya a wajen ki nake son ki bani aron su" gyara zama na yi na ce"Kai kuwa Qalbi me za ka yi da kuɗi har kake kokarin cin bashi?" Sosa keya ya yi ya ce"To dama Mama ce ta tambaye ni kuɗin kuma kin ga wata ya yi nisa" "Nawa kake bukata" na tambaye shi don kar ma ya tsira wani dogon surutu don na riga na san da wata manufar a kasan zuciyar Mama shi ya sa ta tsiro da ya bata kudi "E to ko 100k za su isa" "Kuɗin su na wajen da ka bar su jiya" murmsuhi ya yi ya ce"Dan Allah ki kai mata su kin ga ni na makara" gyaɗa kaina na yi na ce"To zan kai mata" shi kuwa ya fice daga gidan.
Tashi na yi na shiga ɗaki na yi wanka na shirya don zuwa office sai na ciro da kuɗin na je kofar ɗakin Mama na kwankwasa ta bani izinin shigowa.
★Mama Sa'a★
Faɗar baƙin cikin da na kwana da shi a daren jiya ɓata baki ne Allah ne shaida ta ban so ko kaɗan Sumayya ta sake kwana a cikin gidan nan ba, Allah ya sani so na yi ta kwana a gidansu sai dai kuma duk wani shirina ya wargaje ya tashi a tutar babu. Amman idan ta san wata ai ba ta san wata ba na yi alkawari sai ta bar min gidan ɗa ko na yar da ɗan mangwaro na huta da ƙuɗa.
Yau tun safe na kira Jiddah ɗakina na ce"Ki na ji ko Auta" gyaɗa min kai ta yi alamar tana saurare na, sai na ci gaba da cewa"Idan Sumayya ta fito daga ɗakinta ki ce da ita a cikin kuɗin jiya ta baki jika ashirin" "To Mama har ta fito ɗin" haka na tasa keyar su gaba muka nufi falo zaman jiran fitowar Sumayya.
Ga mamakina ko tanka ma Jiddah ba ta yi ba, bare kuma mu saka ran za ta bata kuɗin ko kuma ta faɗi wani abin da zai sa na yi mata masifa tun safe, amman ko kallon arziki ba mu samu daga gare ta ba. Ganin haka ya sa na dawo ɗakina na zauna bayan na hana ta tafiya sama da abinci duk da kuwa na san ba ita za ta ci ba don ta kai wa Abdallah ne, na yi haka ne kawai don ransa ya ɓaci.
Lokacin da ya gama cin abincin ya shigo ɗakina kallon shi na riƙa yi don na ga ko da ɗan ɗigon baƙin ciki ne a fuskar shi na alamar Sumayya ta ɓata mishi rai akan ta ƙi kai mai abinci ɗakinsa. Sai dai kuma shiru babu wani abu da ke nuni da hakan tsaki na ja a cikin raina don wannan lamari ya fara ɓata min rai duk ta inda zan fito sai ta samu hanyar canza akalar abin da na shirya mata.
Murmushi na yi a lokacin da ya tsunguna har ƙasa ya gaishe ni. Cike da fara'a na amsa kafin kuma na ce"Tun ba yau ba na so yi maka magana amman kuma sai na ga yadda kake kokari da mu kar dawainiya ta yi maka yawa" ɗago kansa ya yi cike da biyayya ya ce" Mama me ya faru?" Gyara zamana na yi na ce"Ina son na tambaye ka kuɗi ne amman ina jin nauyin ka" murmushi ya kuma yi min ya ce"Mama idan ba ki tambaye ni na yi miki ba ina anfanin neman da nake yi? Kar ki damu Mama ai kin fi ƙarfin ki bukaci wani abu ki rasa idan dai ina da sauran numfashi a duniya, nawa kike bukata?" Murna fal raina na ce"Jika ɗari nake so" "To Mama zan bada in sha Allah" yana gama faɗa ya tashi don tafiya office.
Da gangan na bukaci haka don na ga kudin da ke hannunta tabbas na san su zai kawo min don da wannan safiyar babu shaka na san ba shi da wannan kudin a hannunsa amman na tambaye shi su.
Bayan kamar minti talatin da fitar Abdallah sai Sumayya ta turo ƙofar ɗakin sallama ɗauke a bakinta ta ce"Mama ga wannan kudin Qalbi ne ya ce na kawo miki su" karɓar kudin na yi ita kuwa ba ta ƙara furta wata kalma ba ta bar min ɗakin. Ina ganin ta fice na tashi tsaye tare da sakin guɗa kamar wadda aka yi wa albishiri ɗin kujerar Makka rawa na fara takawa na ce"Kai ni dai Sa'a na ci sunana wannan uwar sa'a haka abin kam sai godiyar Allah." Ni ɗaya na ci gaba da shagalin murna na raba Sumayya da kuɗin da ban san daga gidan uban wa ta samo su ba. Amman ni dai burina ya cika kuɗin sun dawo mallakina. Hakika raina kan yi baƙi a duk lokacin da na wayi gari na ga Sumayya da wani abu a hannunta, bana son ko kaɗan irin uban kuɗin da Abdallah yake kashe mata, ni da na haife shi ma ba ya min irin wannan hidimar da yake yi wa ƴar gwal ɗin matarsa.
*Cmnts nd share*
[06/12 à 21:33] Émilia: https://chat.whatsapp.com/H9Q7z3J09hnDQuUJNbIdKW
*DA WATA KUSAN...*
NA
Zouley Sabitou (Émilia)
Daga marubuciyar *KUSKURE*
☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSO...☀️
(Home Of Qualités And Trusted Writers Of The Nation)
GA DUK MAI BUKATAR A TALLATA MATA HAJJARTA KOFA A BUƊE TAKE, ZA KU SAMU BIYAN BUKATA.
+22780416252
*Page 04*
Ina isa office na tarar har sun fara meeting wanda Allah ya sani tsabar abubuwan da suka yi min yawa a kaina ya sa na manta da maganar wani meeting. Ganin tabbas dai sun fara ba tare da ni ba sai na shige office ɗina na zauna. Na fara duba wasu files sai bayan sun gama Abdallah ya turo ƙofar office ɗin ya shigo, ɗago kaina na yi na ce"Qalbi kenan dai ba za ka bar shigo min office babu neman izini ko?" Murmushi ya yi ya ce"Ni da office ɗin matata ai babu shamaki a tsakani na da shi" ya faɗa tare da jan kujera ya zauna "Kin ba Mama kuɗin da na ce?" Gyaɗa kai na yi na ce"E na bata" "idan aka yi albashi zan yi miki transfert" "Allah ya kai mu lokacin, Amman Qalbi ba ka ganin wasu ɗawainiyar sun yi maka yawa, ka riƙa rage wa, ka riƙa la'akari da abin da gobe za ta haifar don babu wanda ya san goben sai Allah" ɓata fuska ya yi ya ce"Ban gane ba, Babe me kike nufi? Kuɗin da na ba mahaifiyata shi ne kika fara ƙyashi yanzu kuma?" Girgiza kaina na yi na ce"Allah ya tsare ni yin ƙyashi da matar da take matsayin uwa a wajena" "Idan ba kishi da ƙyashi ba ne ki ke yi da ita, to mene ne?" "Allah ya huci zuciyarka, ban faɗi haka da wata manufa ba illa ma fadar hakan da na yi sai don gobenmu ta yi kyau da ni da kai har da ita Maman" tsaki ya ja kafin ya miƙe tsaye zai bar office ɗin, file ɗin da ya shigo da shi a hannunsa ya ajiye min kafin ya ce"Ga shi nan ki duba idan kin ga dama" ya juya ya bar office ɗin. Aikin gabana na ci gaba da yi kafin na fara duba file ɗin meeting ɗin da suka yi ba tare da ni ba" duk raina a jagule nake jin shi.
Ina cikin aikina sai wayata ta ɗauki ƙara janyo ta na yi ganin sunan jumelle/Twins da alamar Heart/cœur a jiki ya saka na ɗaga tare da yin murmsuhi kamar tana gabana na ce"Madame, ba ki san lokacin aiki ba ne yanzu" daga can bangaren aka amsa min da "Lokacin aiki ai ku ya dama masu Company ba mu ba yan kasuwa" dariya na yi na ce"Kai wannan kasuwancin da a kullum ake yi mana tutiya da shi mu ma shi za mu fara" dariya Rumaisa ta yi ta ce"Mu gani a ƙasa in ji kare" ni ma dariya na yi na ce" ke ma ai yanzu kin faɗa, ya gidan ina princesse?" "Tana lafiya, ina Abdallana?" "Ke kam Rumaisa ba a raba ki da shiririta, yanzu idan Mustapha ya ji ki me za ki ce mishi?" Dariya ta yi ta ce"Ni fa kiranki na yi don na ce miki yau zan zo" "To Allah ya kawo ki lafiya" muka yi sallama na kashe wayar tare da fara haɗa kayana don barin office ɗin. Sakatariyata na kira a waya bayan ta ƙaraso na ce"Ki cire duk wani meeting ɗina na yau ba zan samu damar zuwa ba" da to ta amsa min kafin ta fice daga office ɗin. Ni ma gida na yi wa tsinke ina shiga falon na tarar da Mama a zaune a falo ko sallamar da na yi ba ta amsa ba ta ce"To daga ina kuma? Wannan tafiya dai ba za a ce daga office ba" na ce"Daga office nake Mama" fashewa ta yi da dariya ta ce"Ki nemi karamin yaro ki sanar da shi, don ni dai da hankalina don ba yarda zan yi ba kuma ina sha Allah nan ba da daɗewa ba Abdallah zai gane ainihin fuskar matar da ya aura, wa ya sani ma ko a yawon ta zubar ɗin kika cire mahaifarki ki ka siyar da ita tsabar son abin duniya" tana jan bakinta kafin ta ci gaba da watso min maganganunta masu kama da saukar gwarwashin wuta a cikin zuciyata na fice daga dakin na nufi ɗakina.
Ko da na cire kayana sai na sauko ƙasa na shiga kitchen na haɗa duk wani abun bukata don yin girki na nufi kitchen ɗin da ke bangarena da shi. Sai da na kai kitchen ɗin na manta da ban ɗauko maggi ba ƙasa na kuma sauko wa na ɗauko har na fara taka steps mai zuwa ɓangarena Mama ta ce"Ni kam yau wane irin munafurci ne ake shirin yi da girkin ma ba za a yi a kitchen ɗin falon ba" "Mama zan yi ɓaki ne" "Su waye za su zo? In ce dai ba wannan gayar ɗangin naki ba ne za su zo su cinye wa mutane abinci bayan ga ƴarsu nan a gida da ita da babu duk ɗaya" murmsuhina da ya fi kuka ciwo na yi na ce"A a ba su ba ne za su zo" "To ko da na ji da sauƙi tunda dai ba su ba ne" ɗakina na koma cike da jin haushin maganganunta amman sai na yi kamar babu abin da ya faru na ci gaba da aikin gabana.
★Mama Sa'a★
Yau kam ina falon nan sai na ga munafikin da zai zo gidan ɗana ya ci amanarsa har gida, don wannan munafurcin na Sumayya ban yarda da shi ba idan dai ba yan uwanta ba ne za su zo gidan to kawai kwartonta ne za ta kawo gidan. Ni kuwa ba zan taɓa barin hakan ta faru ba da ya zo gidan zan yi sauri na kira Abdallah ya zo ya ga abin da na daɗe ina faɗa mishi amman ya ƙi yarda da maganata.
Channel ɗin Tv na canza na ci gaba da kallona har Rumana ta shigo falon don sai yanzu ta tashi daga barci na ce"Ke dai Rumanatu kin ji kunya ina dalilin wannan barcin, sai na yi wa ƴaƴanku magana ya samo miki ko da ɗan aiki ne a Companysu" miƙa Rumana ta yi ta ce"Gaskiya dai kam Mama kawai ki yi mishi magana kin ga ni ma zan fara yin ado irin na Sumayya na zama kyakkyawa" wani kallon ba ki da hankali na yi mata kafin na ce"Sai yanzu na san ba ki da hankali ke kam, tsakaninki da Allah ina wani abin mangari da burgewa a jikin Sumayya?" "Tab Mama ai kuwa dai tana da kyau babu laifi" "Ke don Allah shashar banza da wofi da dukan alamu wajen bokan da ta kai Abdallah har da ke suka kai" tashi ta yi ta bar falon tana ta faman yin gunguni. Ban wani kula ta ba na ci gaba da abin da nake yi wato kallon tv da kuma jiran kwarton da Sumayya za ta kawo har gida.
Can aka turo ƙofar falon da sauri na ɗago kaina don ganin mai shigo wa, da ido biyu muka yi da Rumaisa matar Mustapha shi ɗin cousin ɗin su Abdallah ne ta ɓangaren mahaifinsu. Ita kuwa ƴan biyun Sumayya ce da ka ganta ka ga Sumayya kamar an tsaga ƙara, amman ita ko babu komai ta san ciwon kanta. Da sauri na kauda tunanin da yake raina na ce"Maraba, maraba sannu da zuwa" karasowa ta yi cikin falon ta ce"Mama Sa'a barka da wannan lokaci" kafin ta zauna akan daya daga cikin kujerun falon na ce"Yauwa Rumaisa ƴar albarka, ya gidan ina mai babban suna?" "Tana lafiya tana tare da mahaifinta, ina Sumayya?" "Tana ɗakinta" na faɗa ba don na so ba. Miƙe wa tsaye ta yi ta ce"To Mama Sa'a bari na je mu gaisa" daga nan ta fice zuwa sashen Sumayya.
Tsaki na ja a raina na ce"Aikin banza da na san Rumaisa ce bakuwar ai ba zan zauna na ɓata wa kaina lokaci wajen korar sauron da ke shige da fice" ina gama maganar zucina na bar falon zuwa ɗakina na bi lafiyar gado. Don shi kaɗai ne aikin da zan yi a yau dai, Sumayya ta ci albarkacin Rumaisa ni fa da an yi min shawara da cewa zan yi Abdallah ya auri Rumaisa saboda ko babu komai ita ta haifa wa mijinta ƴa kowa ya san ba juya ba ce ya aura sai ni ce dai aka haɗa da jaraba da wannan mai sunan mayun.
★Sumayya★
Ina cikin girkin na ji an buga kofa da karfi alamar rufe ta aka yi, fito wa na yi daga kitchen ɗin na ce"Ikon Allah Rumi ni ban san ranar da za ki zama babba ba" zama ta yi akan sofa ta ce"Kin san Allah ba wani fi na ƙi ka yi ba to ki yi min a hankali" kitchen na koma na ɗauko mata drinks kafin na dawo na ajiye a gabanta. Zama na yi kafin na ce"To mutun dai ko da minti ɗaya ya riga ka zuwa duniya ya girme maka kuma yin biyayya dole ne" bayan ta ɗauki cup ɗin drink din ta ce"Wannan shari'a ina ga sai an je gaban Ummi ita ɗaya ce za ta faɗa miki cewa ni ce babba ki yarda" dariya na yi na ce"To ki saka rana sai mu je gaban Alkali mai girma ummi" drink ɗinta ta shiga sha ni kuwa na koma na duba girkin da na ɗaura kafin na dawo falon wajenta.
"Ina princesse ya aka yi ba ki kawo min ita ba?" "Tana wajen Mustapha mana tare suka tafi office ai" kallonta na yi na ce"Ikon Allah yau kuma sunan mijin kai tsaye aka kira babu ko kara, faɗan min laifin me kuma ya yi?" Don duk ranar da Rumaisa za ta kira sunan mijinta haka kai tsaye babu shakka ya yi mata wani abin ne, taɓe baki ta yi ta ce"Ya fara sha min kai ne da maganar haihuwa ni kuma gaskiya ba kaza ba ce, duka ma shekarun Aisha nawa ne?" Ajiyar zuciya na sauke kafin na matso kusa da ita cikin sigar rarrashi na ce"Haba Rumi kar ce haka mana, wasu fa neman haihuwar suke ido rufe ba su samu ba, ki tsaida shan maganin haka tunda dai har mijinki ne ya bukata" wani kallo ta yi min kafin cikin halin ko in kula ta ce" To sai